5 Oktoba 2020 - 11:46
Shugaban Kasar Iran Ya Aike Wa Da Sabon Sarkin Kuwaiti Sakon Taya Murna

Shugaba Hassan Rauhani ya fada a cikin wasikar da ya aike wa sabon sarki Kuwait Sheikh Nawwaf al-Ahmad al-Jabir aj-Sabah, cewa; A karkashin ci gaba da aiki da tafarkin hikima, alakar ‘yan’uwantaka a tsakanin kasashenmu biyu za ta ci gaba da bunkasa kamar yadda ta kasance a baya, za kuma mu ga ci gaba da samun zaman lafiya a cikin wannan yankin.

ABNA24 : Shugaban kasar ta Iran ya ci gaba da cewa; Muna taya ku murna saboda karbar jagorancin kasar Kuwaiti wacce kawa ce kuma ‘yar’uwa ga Iran.

A ranar Larabar da ta gabata ne dai sabon sarkin na Kuwaiti Nawwaf al-Ahmad, al-Sabah ya yi rantsuwar kama aiki a gaban majalisar kasar a matsayin wanda ya gaji sabah al-Ahamd, al-sabah, wanda ya rasu a ranar 29 ga watan Satumba da ya shude.

Tun da fari, ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jadaw Zarif ya kai ziyarar aiki kasar ta Kuwaiti a jiya Lahadi, inda ya gana da sabon sarkin.

342/